Jam’iyyar PDP a Jihar Gombe ta yi watsi da zaɓen fidda gwani da wani ɓangare a jam’iyyar ya gudanar, inda ta bayyana lamarin a matsayin haramtacce kuma barazana ga zaman lafiya da kwanciyar hankalin jam’iyyar.
A cikin wata sanarwa da Sakataren Yada Labarai na jam’iyyar na jiha, Abdulkadir Ahmad Dukku, ya sanyawa hannu kuma ya miƙawa Jewel Times Hausa, jam’iyyar ta ce a ƙarƙashin jagorancin Sanata Ibrahim Hassan Dankwambo (Talban Gombe) da Shugaban jam’iyyar na jihar, Manjo Janar Amnon Kalaye Kwaskebe (mai ritaya), jam’iyyar tana nan a kan bakanta cewa ta riga ta kammala duk zabukan fidda gwani a fadin jihar.
Da suke jaddada cewa jam’iyyar ta kasance “tsintsiya maɗaurinki daya ba tare da wani ɓangare ba a jihar,” jagororin sun bayyana cewa “ba za su zuba ido suna kallon wassu ɓatagari su haifar da ruɗani a cikin jam’iyyar ba.”
Don haka, PDP ta bayyana cewa ba ruwanta da wancan zaɓen da ya sabawa tsarin mulkin jam’iyyar, inda ta kwatanta su da “barazana ga haɗin kan jam’iyyar dama demokraɗiyya baki ɗaya.”
Shugabannin sun kuma jaddada cewa tsarin tantance ƴan takara na dukkan muƙaman siyasa ya riga ya kammala, wanda kuma ya tabbatar da da Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami a matsayin ɗan takaran gwamna ɗaya tilo na jam’iyyar a zaɓen 2027.
Dangane da haka, jam’iyyar ta yi ƙira ga duk masu ruwa da tsaki, mambobi, magoya baya, da sauran jama’a cewa “su yi watsi da harkokin irin waɗancan marasa kishin ƙasa, waɗanda ba sa son ci gaba da walwalar al’ummar Gombe.”
Wannan jawabi dai na zuwa ne a matsayin wani martani kai tsaye ga rahotannin dake yawo game da wani ɓangare na jam’iyyar ƙarƙashin jagorancin Tanimu Turaki dake goyon bayan Ahmad Yayari a matsayin ɗan takaran gwamnan Gombe, wani mataki da shugabannin jam’iyyar na jihar suka fito fili suka soka tare da bayyana shi a matsayin aikin banza.

