Skip to content
Jewel Times
Menu
  • Gombe Social Investment Coordinator Visits Progress Radio, Seeks Collaboration
  • Sample Page
Menu

Kungiyoyin Fararen Fula 15 A Gombe Sun Janye Kudurin Shiga Zanga-zanga

Posted on July 29, 2024 by Jtimes

 

Daga Yunusa Isa, Gombe

 

Gamayyar ƙungiyoyin farar hula 15 a Jihar Gombe sun janye Ƙudurinsa na shiga zanga-zangar da ake shirin yi a faɗin ƙasar nan daga ranar 1 zuwa 10 ga watan Agustan 2024.

 

Gamayyar ƙungiyoyin ta bayyana hakan ne yayin wata ganawa da manema labarai a ƙarshen taron da suka yi mai taken “Bita kan tsaro da zanga-zangar da aka tsara yi a faɗin ƙasar”.

Da yake zantawa da manema labarai a yayin taron, jagoran gamayyar ƙungiyoyin Dr Habeeb Muhammad, yace “Bayan gudanar da taruka da tuntuɓar juna da shugabannin addini, da sarakuna, da ƙungiyoyi, da ɗaiɗaikun jama’a da hukumomin tsaro, mun yanke shawarar janyewa daga zanga-zangar da aka tsara yi a faɗin ƙasar nan”.

 

Dokta Habeeb yace “Wassu dalilan da suka ƙara gamsar da mu mu janyewa daga zanga-zangar, sun haɗa da rashin sanin shugabannin dake jagorantar zanga-zangar, da kuma yiwuwar sauya akalarta ya zuwa tarzoma don haddasa matsalar tsaro”.

Sai dai don hana afkuwar zanga-zangar da aka shirya yi, ƙungiyoyin sun shawarci gwamnati ta ɗauki kwararan matakan magance matsalar rashin tsaro, da wahalhalun rayuwa da ake fama da su, da farfaɗo da matatun mai, da dawo da tallafin man fetur dana wutar lantarki, da rage kuɗaɗen makaranta a manyan makarantu, da rage yawan kudaden da ake kashewa kan gudanar da gwamnati, da rage haraji da kaso 50 cikin ɗari, da kuma aiwatar da sabon mafi ƙarancin albashi yadda ya kamata.

Gamayyar ta yi watsi da zargin da ake yi na cewa gwamnati ce ke ɗaukar nauyinta don sukurkutar da zanga-zangar, tana mai tabbatar da cewa lafiya da tsaro da jin daɗin jama’a su ne manyan abubuwan da suka fi damuwa da su.

 

Dr Habeeb ya ƙara da cewa zanga-zangar ba lallai ne ta haifar da ɗa mai ido ba idan ba a yi hankali ba, duba da abubuwan da suka faru a wassu ƙasashen Afirka.

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recent Posts

  • Zulum Donates, Commissions New Staff Quarters at Federal University of Health Sciences Azare
  • FRSC Declares War on Indiscipline, Deploys Senior Officers to Restore Professionalism
  • Bala Wunti Support Organisation Empowers Blind, Deaf with Entrepreneurial Skills
  • NEDC Bolsters Journalists’ Welfare with Ramadan Food Support
  • Ramadan: BWSO Donates Cash, Food Items to People with Disabilities in Bauchi

Recent Comments

  1. A WordPress Commenter on Hello world!

Archives

  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • June 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • February 2025
  • January 2025
  • December 2024
  • November 2024
  • October 2024
  • September 2024
  • August 2024
  • July 2024
  • June 2024
  • May 2024
  • April 2024
  • March 2024
  • February 2024

Categories

  • Agriculture
  • Anti Corruption
  • Article/Opinion
  • Cybercrime
  • Economy
  • Education
  • Environment
  • Governance
  • Health
  • Infrastructure
  • News
  • Nutrition
  • Opinion
  • Politics
  • Religion
  • Rural Development
  • Security
  • Tradition
  • Transportation
  • Uncategorized
  • Urban Development
  • Urban Development
  • Women
  • Youths
©2026 Jewel Times | Design: Newspaperly WordPress Theme