Skip to content
Jewel Times
Menu
  • Gombe Social Investment Coordinator Visits Progress Radio, Seeks Collaboration
  • Sample Page
Menu

Gombe 2027: Farfesa Pantami Ne Magajin Inuwa, A Cewar Wata Kungiyar Magoya Baya

Posted on March 5, 2024March 5, 2024 by Jtimes

Daga Abubakar Rabilu, Gombe

Wata ƙungiyar matasa dake fafutukar kawo sauyi a Jihar Gombe mai suna ‘North East Coalition of Youth for Progressive Governance and Sustainable Development’ ta bayyana cewa a 2027 Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami ne zai gaji kujerar Inuwa.

Ƙungiyar ta bayyana hakan ne ta bakin Gidion Musa, wadda ya ce ƙungiyar tana kira ga tsohon Ministan Sadarwa da Tattalin arziki Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami da ya amsa ƙiransu a 2027 wajen fitowa takarar gwamana a jihar, yana mai cewa shi yafi cancantar ya gaji kujerar daga Gwamna Muhammad Inuwa Yahaya.

Gideon Musa, ya bayyana hakan ne yayin wani taron manema labarai da suka ƙira a Gombe suna masu ƙira ga Pantami da cewa ya amsa ƙiransu.

Yace sun amincewa tsohon ministan ne sakamakon ɗimbin nasarorin da ya samu a lokacin da ya zama darakta a Hukumar Bunƙasa Fasahar Sadarwa ta Ƙasa (NITDA) da kuma lokacin da yake ministan Sadarwa da Tattalin Arziki na Zamani.

A cewar ƙungiyar, Pantami ya samarwa al’ummar Jihar Gombe damar amfana da fasahar zamani ta hanyar buɗe cibiyoyin fasahar sadarwar zamani (ICT) a makarantu da sassa daban-daban na jihar inda ake horar da jama’a tare da ba su damar shiga yanar gizo kyauta.

“Farfesa Pantami ne ya jagoranci samar da ofisoshi a faɗin ƙasar nan ciki har da nan Jihar Gombe, tsohon ministan ya samar da ci gaba da damammakin ayyukan fasaha a yankin arewa maso gabas”.

Ƙungiyar ta ƙara da cewa “Waɗannan ofisoshin ba kawai sun inganta haɗin guiwa ba ne, sun ma taimakawa ma’aikatan jihar wajen samun ƙarin dama don haɗin guiwa da dandalin ƙirƙiro da musayar bayanai.”, in ji shi.

Ta buƙaci tsohon ministan ya amince da kiran da ta yi masa na tsayawa takaran gwamnan Jihar ta Gombe a zaɓe mai zuwa na shekarar 2027 sannan suka buƙaci Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya ya mara masa baya a matsayin wanda zai gaje shi.

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recent Posts

  • BOGIS Directs Land Owners To Link NIN With Certificates Of Occupancy
  • Gombe Wins 10th Edition of NILDS Zonal Quiz Competition
  • Gombe Civil Service Commences Staff Verification, Aims Digital Database
  • Merit and Vibes Awards 2025 Celebrates Excellence, Promotes Inclusion in Creative Industry
  • Gombe Adopts Digital Technology to Improve Education Data Collection for 2024/2025 School Census

Recent Comments

  1. A WordPress Commenter on Hello world!

Archives

  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • June 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • February 2025
  • January 2025
  • December 2024
  • November 2024
  • October 2024
  • September 2024
  • August 2024
  • July 2024
  • June 2024
  • May 2024
  • April 2024
  • March 2024
  • February 2024

Categories

  • Agriculture
  • Anti Corruption
  • Article/Opinion
  • Cybercrime
  • Economy
  • Education
  • Environment
  • Governance
  • Health
  • Infrastructure
  • News
  • Nutrition
  • Opinion
  • Politics
  • Religion
  • Rural Development
  • Security
  • Tradition
  • Uncategorized
  • Urban Development
  • Urban Development
  • Women
  • Youths
©2025 Jewel Times | Design: Newspaperly WordPress Theme