Skip to content
Jewel Times
Menu
  • Gombe Social Investment Coordinator Visits Progress Radio, Seeks Collaboration
  • Sample Page
Menu

Gobara Ta Lakume Rumbun Adana Magunguna Na Gombe, Dauke Da Magunguna Da Kayayyakin Jinya Na Biliyoyin Naira

Posted on February 19, 2024February 19, 2024 by Jtimes

Daga Yunusa Isa, Gombe

Wata Gobara data tashi da tsakar dare wayewar yau Litinin ta ƙona ɗaya daga cikin rumbunan magunguna na Ma’aikatar Lafiyar Jihar Gombe, lamarin da ya haddasa asarar magunguna da allurai da kayayyakin jinya na biliyoyin Naira.

Da yake zantawa da manema labarai yayin ziyarar ganewa idonsa abinda ya faru, Kwamishinan Lafiya na Jihar Dr Habu Ɗahiru yace gobarar ta tashi ne da misalin ƙarfe 2:00 na dare wayewar yau Litinin.

Yace “Ma’aikatan dake bakin aiki sun yi gaggawar sanar da jami’an dake kula da rumbunan, inda suma nan take suka sanar da ‘yan kwana-kwana don kai ɗaukin gaggawa, amma kafin ‘yan kwana-kwanan su isa, gobarar ta yi barna sosai, wanda har ya kai ga rugujewar katangar rumbun ta ɓarin gabas”.

Kwamishinan yace ana ci gaba da gudanar da bincike don gano musabbabin gobarar da girman barnar da ta yi.

Ya ƙara da cewa, duk da lalata magungunan da za a yi amfani da su don rigakafin cutukan dake kashe yara a watan Maris mai zuwa kamar sanƙarau da Polio, gwamnatin jihar ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen tabbatar da nasarar rigakafin.

Dokta Habu Ɗahiru yace ma’aikatar za ta gaggauta tuntuɓar Gwamnatin Tarayya da ƙungiyoyin bada tallafi don cike giɓin da aka samu sanadiyyar gobarar.

A nasa ɓangaren, Daraktan Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Gombe wanda jami’in aikace-aikacen hukumar Umar Faruk ya wakilta, yace sun samu ƙiran waya na gaggawa da misalin ƙarfe 3:08 na dare, kuma nan take suka garzaya wurin.

Yace ‘yan kwana-kwanan sun samu nasarar shawo kan gobarar ta hanyar magance ci gaba da yaɗuwarta zuwa sauran sassan rumbunan.

Da yake zargin wutar lantarki da haddasa gobarar, jami’in kashe gobaran yace nan ba da daɗewa ba hukumar za ta yi wa manema labarai bayani idan ta kammala bincike.

Sai ya buƙaci ma’aikatu da hukumomi su riƙa horar da ma’aikatansu yadda za su yi amfani da kayayyakin kashe gobara yayin buƙatar gaggawa.

Har ya zuwa yammacin yau Litinin hayaƙi na ci gaba da tashi a wassu sassan rumbun.

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recent Posts

  • Parents Encouraged to Support Nursing Students
  • Gombe’s Infrastructure Push: Works Commissioner Highlights Benefits of Key Projects
  • Gombe Govt Efforts Paying Off as Farmer-Herder Clashes Minimised — Agric Commissioner
  • Muhammadu Buhari Industrial Park Takes Shape with 12 Companies on Site, 14 on Queue
  • Gombe Governor Commissions POWA Model School in Sum, Bauchi State

Recent Comments

  1. A WordPress Commenter on Hello world!

Archives

  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • February 2025
  • January 2025
  • December 2024
  • November 2024
  • October 2024
  • September 2024
  • August 2024
  • July 2024
  • June 2024
  • May 2024
  • April 2024
  • March 2024
  • February 2024

Categories

  • Agriculture
  • Article/Opinion
  • Cybercrime
  • Economy
  • Education
  • Environment
  • Governance
  • Health
  • Infrastructure
  • News
  • Nutrition
  • Politics
  • Religion
  • Rural Development
  • Security
  • Tradition
  • Uncategorized
  • Urban Development
  • Urban Development
  • Women
  • Youths
©2025 Jewel Times | Design: Newspaperly WordPress Theme