Skip to content
Jewel Times
Menu
  • Gombe Social Investment Coordinator Visits Progress Radio, Seeks Collaboration
  • Sample Page
Menu

Tekan Peace Desk Ta Bukaci Gombawa Su Girmama Addinan Juna Da Kare Hakkin Dan Adam

Posted on March 21, 2024 by Jtimes

Daga Yunusa Isa, Gombe

An jaddada buƙatar al’ummar Jihar Gombe su mutunta aƙidar juna, da kare hakkin bil-adama tare da taimakawa juna.

Babban jami’in da ya gabatar da maƙala Dr Obadiah Samuel na Jami’ar Jos ne ya jaddada buƙatar hakan yayin wani taron tuntuɓa na masu ruwa da tsaki kan haƙƙin ɗan-adam da mutunta addinan juna, wanda Tekan Peace Desk ta shirya a Gombe.

Da yake gabatar da maƙala mai taken “Mu Fahimci Matsalar Rashin Mutunta Addini da Tasirinsa Kan Kare Haƙƙoƙin Ɗan-Adam” da kuma wata maƙalar mai taken “Hanyoyin Samar da Mafita Don Kare Haƙƙoƙin Ɗan-Adam”, Obadiah yace girmama addinan juna yana da nasaba da mutunta aƙidar wassu da kuma gujewa duk wani abu da ka iya tunzurasu.

Da yake ƙarfafa gwiwar al’ummar jihar su ci gaba da zama ’yan uwan juna, jami’in yace haƙuri da girmama addinan juna yana kawo zaman lafiya, haɗin kai da ci gaban ƙasa.

Dangane da kare haƙƙin ɗan-adam, Dr Obadiah yace yarjejeniyoyin ƙasa, dana nahiyoyi dana ƙasa da ƙasa sun amince da yancin rayuwa, da yancin addini ga kowa, yana mai cewa ya zama wajibi ga ɗaiɗaikun jama’a da kasashe su mutunta tare da kiyaye waɗannan haƙƙoƙi.

Ya buƙaci mahalarta taron su zama jakadun zaman lafiya ta hanyar isar da ilimin da suka samu a yayin taron ga waɗanda basa wurin.

Wassu daga cikin mahalarta taron da suka haɗa da Lami Andrew da Ali Alola Alfinti, sun bayyana jahilci da fatara da son zuciya irin na siyasa da tsattsauran ra’ayi a matsayin manyan ababen dake haddasa rashin mutunta addinan juna a jihar.

Sai dai sun bayyana ƙauna, da ilimi, da wayar da kan jama’a da fahimtar juna da kuma yaƙi da fatara a matsayin hanyoyin magance rashin girmana addinan juna da take haƙƙin ɗan-adam. Sun kuma ba da tabbacin isar da ilimin da suka ƙaru da shi zuwa ga wassu.

Tekan Peace Desk tare da tallafi daga Brot da Tarayyar Turai suna aiwatar da wani shiri ne mai take ‘Addini don Aminci’ a wassu garuruwa shida; biyu a kowace karamar hukuma na Kwami, da Yamaltu Deba da kuma Ɓillliri.

Shirin yana maida hankali ne wajen baiwa masu ruwa da tsaki damar inganta zaman lafiya, da kare haƙƙin ɗan-adam, da demokraɗiyya da kuma mutunta addinan juna a Najeriya.

Waɗanda da suka halarci taron sun haɗa da ƙungiyoyin al’umma dana addinai dana fararen fula, da ma’aikatan kafafen yaɗa labarai, da jami’an gwamnati da hukumomin tsaro da kuma masu fafutukar kare haƙƙin bil’adama.

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recent Posts

  • Parents Encouraged to Support Nursing Students
  • Gombe’s Infrastructure Push: Works Commissioner Highlights Benefits of Key Projects
  • Gombe Govt Efforts Paying Off as Farmer-Herder Clashes Minimised — Agric Commissioner
  • Muhammadu Buhari Industrial Park Takes Shape with 12 Companies on Site, 14 on Queue
  • Gombe Governor Commissions POWA Model School in Sum, Bauchi State

Recent Comments

  1. A WordPress Commenter on Hello world!

Archives

  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • February 2025
  • January 2025
  • December 2024
  • November 2024
  • October 2024
  • September 2024
  • August 2024
  • July 2024
  • June 2024
  • May 2024
  • April 2024
  • March 2024
  • February 2024

Categories

  • Agriculture
  • Article/Opinion
  • Cybercrime
  • Economy
  • Education
  • Environment
  • Governance
  • Health
  • Infrastructure
  • News
  • Nutrition
  • Politics
  • Religion
  • Rural Development
  • Security
  • Tradition
  • Uncategorized
  • Urban Development
  • Urban Development
  • Women
  • Youths
©2025 Jewel Times | Design: Newspaperly WordPress Theme