
Daga Yunusa Isa, Gombe
Rundunar Tsaro ta Civil Defence, ta kama wassu mutane shida da ake zargi da ƙwaƙule idon Marigayi Malam Manu Wanzam na Garin Gaɗam dake Ƙaramar Hukumar Kwami.
Da yake gabatar da waɗanda ake zargin yau Juma’a a madadin kwamandan hukumar a jihar, Jibrin Idris, Jami’in Hulɗa da Jama’a na rundunar SC Buhari Sa’ad yace bayan samun bayanan sirri, jami’an rundunar na Gaɗam sun yi nasarar cafke waɗanda ake zargin a wani samame na haɗin gwiwa a ranar 11 ga wannan wata.

“Mun kama waɗanda muke zargin ne da laifin tone kabarin Marigayi Mallam Manu Wanzam, ɗan shekaru 85 mazaunin Gaɗam wanda aka binne a ranar 9 ga watan Satumban 2025 a Maƙabartar Gadam ta Arewa. Waɗanda ake zargin sun haɗa da: Adamu Umar ɗan shekaru 22, Umar Jibrin Aboki ɗan shekaru 21, Abdullahi Umar Dauda mai shekaru 17, da Muhammad Isa Chindo mai shekaru 28, sai Kawuji Sarki mai shekara 39, da Manu Sale mai shekaru 23. waɗanda ake zargin suna zaune ne a anguwanni daban-daban duk a Ƙaramar ta Kwami”.
Jami’in yace bincike ya nuna cewa Kawuji Sarki ne ya bada kwangilar aika-aikar ga Muhammed Isa Chindo, wanda shi kuma ya bada aikin ga sauran waɗanda ake zargin don tono kabarin da cire idanun, bisa alkawarin baiwa kowanne kuɗi Naira dubu 500 kowanne.
PROn ya ƙara da cewa “Saboda haka, waɗanda ake zargin suka haɗa baki tare da tono gawar, inda suka ƙwaƙule idanun marigayin, suka kuma sake binneta”.

Yace yayin da waɗanda ake zargin suka amsa laifin da ake zarginsu da aikatawa, rundunar tana ƙoƙarin cafko ɗaya babban mai laifin wadda ari ta kare, yana mai tabbatar da cewa da zarar an kammala bincike za a gurfanar da su gaban ƙuliya.
Da yake tabbatarwa jama’a ƙudurin rundunar ta Civil Defence na kare rayuka da dukiyoyi, kwamandan ya yabawa jama’a bisa yadda suke baiwa jami’an tsaro muhimman bayanan tsaro dake taimakawa wajen daƙile miyagun laifuka a jihar.
Ya kuma buƙaci al’ummar jihar su kasance a ankare, tare da kai rahoton duk wani abinda basu gamsu da shi ba ga jami’an tsaro mafi kusa, ko kuma su ƙira layukan neman ɗaukin gaggawa na rundunar: 08060737200, 08027370023, 08069135023, 08038392661, 08069514557.
