Daga Yunusa Isa, Gombe
Tsohon Mataimakin Shugaban Kasa Alhaji Atiku Abubakar, ya samu gagarumar nasara a zaɓen fidda gwani na takarar shugaban ƙasa na Jam’iyyar ADC a Jihar Gombe, inda ya lallasa abokan takararsa, Rotimi Amaechi da Muhammad Hayatuddeen Adamu da tazara mai ɗimbin yawa.
Da yake sanar da sakamakon a hukumance bayan tattara sakamakon ƙananan hukumomi 11 na jihar, Shugaban Kwamitin Zaben Fidda Gwanin na ADC a Jihar Gombe, Farfesa David Agbu, ya tabbatar cewa Atiku ya kada abokan karawar tasa biyu Amaechi da Hayatuddeen warwas.
Bisa ga alƙaluman da Farfesa Agbu ya bayyana a hukumance, Atiku ya samu nasara da kuri’u 139,334. Yayinda Rotimi Amaechi ya samu kuri’u 1,150, Hayatuddeen kuwa ya zo na ƙarshe da ƙuri’u 465.
“Bayan samun mafi yawan ƙuri’un da aka kaɗa, kuma ya cika dukkan sharuɗan da doka ta tanada, kwamitinmu ya gamsu cewa Atiku Abubakar ne ya samu mafi yawan ƙuri’un da aka kaɗa, kuma mun bayyana shi a matsayin wanda ya yi nasara, a zaɓen fidda gwani na shugaban kasa na jam’iyyar ADC a Jihar Gombe,” in ji Farfesa Agbu.
Haka zalika, shugaban kwamitin ya yaba da yadda aka gudanar da zaɓen cikin tsari, yana mai cewa “Zaɓen ya kasance cikin lumana, gaskiya, adalci, da kuma nagarta a dukkanin gundumomi 114 na jihar”.
Yanayin ƙuri’un da aka kaɗa ya nuna yadda zaɓen ya kaya a ƙananan hukumomi 11 inda Atikun ya mamaye jihar:
A Ƙaramar Hukumar Gombe: Atiku ya samu ƙuri’u 27,800, yayin da Amaechi ya samu 376, Hayatuddeen kuma ya samu 40.
A Yamaltu-Deba: Atiku ya lashe kuri’u 20,367, inda ya bar Amaechi da kuri’u 5, Hayatuddeen kuma 4.
A Ƙaramar Hukumar Akko ma Yanayin bai canza ba, inda Atiku ya samu ƙuri’u 17,218, yayin da Amaechi ya samu 308, Hayatuddeen kuwa ya samu ƙuri’u 50.
Atiku ya kuma samu makamanciyar wannar nasara da gagarumar tazara a sauran ƙananan hukumomin jihar kamar haka:
Kwami: (Atiku 13,973; Amaechi 11; Hayatuddeen 5).
Funakaye: (Atiku 13,323; Amaechi 14; Hayatuddeen 5).
Kaltungo: (Atiku 10,853; Amaechi 28; Hayatuddeen 16).
Balanga: (Atiku 8,958; Amaechi 270; Hayatuddeen 80).
Billiri: (Atiku 8,086; Amaechi 208; Hayatuddeen 202).
Dukku: (Atiku 7,636; Amaechi 38; Hayatuddeen 27).
Shongom: (Atiku 5,678; Amaechi 51; Hayatuddeen 21).
Nafada: (Atiku 5,416; Amaechi 21; Hayatuddeen 5).
Wannar gagarumar nasara ta sake tabbatar da cewa Gombe sananniyar cibiyar magoya baya ce ga tsohon Mataimakin Shugaban Kasar.
Wannan rinjaye da Atiku ya samu a jihar ta yi kama da wacce ya samu a babban zaɓen da ya gabata, inda ya doke shugaba Bola Ahmed Tinubu, da gagarumar tazara.

