Skip to content
Jewel Times
Menu
  • Gombe Social Investment Coordinator Visits Progress Radio, Seeks Collaboration
  • Sample Page
Menu

Gwamnatin Gombe Ta Karbi Bukatun Yan Kwangila Don Gina Cibiyoyin Rukunan Gwamnati Uku

Posted on March 4, 2024March 4, 2024 by Jtimes

Daga Yunusa Isa, Gombe

Ma’aikatar Ayyuka, Gidaje da Sufuri ta Jihar Gombe ta karɓi buƙatun kamfanonin kwangila guda bakwai, waɗanda ke neman ayyukan gina sabin cibiyoyin rukunan gwamnati uku, da suka haɗa da Majalisar Dokokin Jiha, da Rukunin ɓangaren Shari’a da kuma Sakatariyar Jiha.

Da yake jawabi yayin bikin miƙa buƙatun kamfanonin a ma’aikatar, Kwamishinan Ayyuka, Gidaje da Sufuri Injiniya Usman Maijama’a Kallamu ya tabbatarwa ‘yan kwangilan aniyar ma’aikatar na yin adalci da daidaito wajen nazarin buƙatun da suka gabatar kafin zaɓan waɗanda zasu yi nasara.

Maijama’a wanda ya samu wakilcin Babban Sakataren Ma’aikatar Idris Yanbiyu Buba, ya buƙaci duk ‘yan kwangilan da suka yi nasara su tsaya kan ka’idojin kwangilolin, tare da kammala su akan lokaci.

Ya kuma yabawa Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya bisa hangen nesansa na gina cibiyoyin rukunan gwamnatin uku, yana mai cewa idan aka kammalasu, Gombe za ta kasance tauraruwar jiha wacce za a yi ta koyi da ita a ƙasar nan.

Tun farko a nasu jawaban, wakilan ’yan kwangila, dana ƙungiyoyin fararen fula, da wakilin ofishin bin ka’idoji a harkokin gwamnati, da kuma Babban Mataimaki na Musamman ga Gwamnan Jihar kan Ayyuka na Musamman Architect Yakubu Mamman, sun yaba da tsarin neman kwangilolin, suna masu bayyana shi a matsayin wadda aka yi cikin gaskiya da adalci.

Suka ce ba za ce ga wadda ya yi asara ba a ƙarshen lamarin, saboda ’yan kwangila suna ɗaukar kansu a matsayin iyali guda.

Sun yabawa ma’aikatar ayyukan bisa yadda a kullum take bin tsari a harkokinta yadda ya dace, suna masu ƙira ga sauran ma’aikatu su yi koyi da ita.

Kamfanonin bakwai da suka gabatar da bukatun su na yin ayyukan uku sune: KIPS ENGINEERING LTD, da TERN GLOBAL, da KASH CONSTRUCTION NIG LTD, da BMC, da A&K NIG LTD, da SUJECT CONSTRUCTION NIG LTD, da kuma UTMOST NIG LTD.

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recent Posts

  • Minority Whip Ali Isa JC Dumps PDP, Cites Undemocratic Principles as Reasons
  • GOSUPDA Warns Gombe Residents Against Payment on Sites, Says All Payments Must go Through TSA
  • Alkali Bows Out of Gombe Budget Ministry, Cites Policy Wins
  • Bauchi Govt Commences Construction of Perimeter Fence in GSSS Gamawa 
  • Gombe Governor Lauds Gender Inclusion as Lafarge Graduates 20 Female Truckers in Ashaka

Recent Comments

  1. A WordPress Commenter on Hello world!

Archives

  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • June 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • February 2025
  • January 2025
  • December 2024
  • November 2024
  • October 2024
  • September 2024
  • August 2024
  • July 2024
  • June 2024
  • May 2024
  • April 2024
  • March 2024
  • February 2024

Categories

  • Agriculture
  • Anti Corruption
  • Article/Opinion
  • Cybercrime
  • Economy
  • Education
  • Environment
  • Governance
  • Health
  • Infrastructure
  • News
  • Nutrition
  • Opinion
  • Politics
  • Religion
  • Rural Development
  • Security
  • Tradition
  • Transportation
  • Uncategorized
  • Urban Development
  • Urban Development
  • Women
  • Youths
©2026 Jewel Times | Design: Newspaperly WordPress Theme