Skip to content
Jewel Times
Menu
  • Gombe Social Investment Coordinator Visits Progress Radio, Seeks Collaboration
  • Sample Page
Menu

Samar Da Abinci: NEDC Ta Bada Tallafin Kayan Aiki Da Sinadaran Noma Ga Gwamnatin Gombe Da Sanatoci Uku Don Inganta Noman Rani

Posted on April 5, 2024 by Jtimes

Daga Yunusa Isa, Gombe

Hukumar Raya Yankin Arewa Maso Gabas (NEDC) ta miƙa tallafin kayan noma ga Gwamnatin Jihar Gombe da sanatoci uku na Gombe ta Arewa, Gombe ta Tsakiya da Gombe ta Kudu.

Da yake jawabi yayin miƙa kayayyakin a Gombe, Muƙaddashin Ko-odinetan Hukumar Raya Yankin na Arewa Maso Gabas a Jihar Gombe, Rufa’i Lawan Baba Manu, yace an ɗauki matakin ne don aiwatar da shirin shugaban ƙasa na inganta samar da abinci a Jihar Gombe, Arewa maso gabas da Najeriya baki ɗaya.

Yace “Kamar yadda kuka sani, aniyar mu ne mu bunƙasa noman rani, don haka burinmu shi ne mu haɗa kai da gwamnatin jiha da sauran masu ruwa da tsaki don ganin mun tallafawa manoma kai tsaye ba tare da wani cikas ba.”

Ya kuma bayyana ƙwarin gwiwar cewa gwamnatin jihar ƙarƙashin Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya za ta yi adalci wajen tabbatar da an yi amfani da kayan aiki da sinadaran yadda ya kamata don samun sakamako mai kyau.

Ya yi ƙira ga manoman da za su amfana su ɗauki wannan tallafi a matsayin wata babbar dama ta bunƙasa sana’arsu, yana mai tabbatar da cewa sun samar da hanyoyin bibiya da sanya ido don tabbatar da cewa ba a karkatar da kayayyakin ba.

Da yake jawabi a madadin gwamnatin jihar, wakilin kwamishinan noma da kiwo na jihar Mista Jonathan Bulus, da Wakilin Sanata Ibrahim Hassan Dankwambo, Sanata mai wakiltar Gombe ta Arewa Hassan S. Dogarai, sun yabawa hukumar ta NEDC bisa wannan tallafi, suna masu tabbatar da cewa matakin zai taimakawa ƙoƙarinsu wajen samar da wadataccen abinci a jihar.

Kwamishinan ya bada tabbacin cewa za a tabbatar kayan aiki da sinadaran noman sun kai ga manoman ainihi a jihar, yana mai cewa matakin zai taimaka matuka wajen inganta manoman rani.

Yace akwai wurare kimanin 46 da ake noman rani bana a faɗin Jihar Gombe.

Bulus ya ƙara da cewa kasancewar Jihar Gombe jihar manoma, wannan tallafi ya zo a lokacin da ya dace musamman ga manoman rani, waɗanda yace za su iya amfani da kayan aikin wajen inganta nomansu na damina idan aka samu fari.

Kayayyakin noma da sinadaran da hukumar ta NEDC ta baiwa gwamnatin jihar sun haɗa da taki na ruwa lita 2000, da urea lita 1000, da maganin feshin ciyawa lita 3000, da kuma injunan ban ruwa guda 500.

A ɗaya ɓangaren kuma, kowanne daga cikin sanatocin jihar uku ya samu taki NPK lita 300, da urea lita 200, da maganin feshin ciyawa lita 700, da injunan ban ruwa guda 100 da kuma tukwanen girki guda 50 don rabawa ga al’ummomin mazaɓunsu.

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recent Posts

  • 2027: Coalition Endorses Dr. Suleiman for Bauchi Governorship
  • Obasanjo, Inuwa Commissions Ultramodern Premier Seeds Industry at Muhammadu Buhari Industrial Park
  • JED Management Commiserates With Governor Yahaya Over Tudunwadan Pantami Tragedy
  • Bauchi Allied Conservative Congress Organizes Party’s Stakeholders Meeting
  • Bala Mohammed’s Leadership Model Seen as Symbol of Hope on Democracy Day

Recent Comments

  1. A WordPress Commenter on Hello world!

Archives

  • June 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • February 2025
  • January 2025
  • December 2024
  • November 2024
  • October 2024
  • September 2024
  • August 2024
  • July 2024
  • June 2024
  • May 2024
  • April 2024
  • March 2024
  • February 2024

Categories

  • Agriculture
  • Article/Opinion
  • Cybercrime
  • Economy
  • Education
  • Environment
  • Governance
  • Health
  • Infrastructure
  • News
  • Nutrition
  • Politics
  • Religion
  • Rural Development
  • Security
  • Tradition
  • Uncategorized
  • Urban Development
  • Urban Development
  • Women
  • Youths
©2025 Jewel Times | Design: Newspaperly WordPress Theme