Skip to content
Jewel Times
Menu
  • Gombe Social Investment Coordinator Visits Progress Radio, Seeks Collaboration
  • Sample Page
Menu

Magance Hatsura: Gwamna Inuwa Ya Yi Kiran A Gyara Hanyoyin Arewa Maso Gabas, Ya Yabawa Kokarin Hukumar FRSC

Posted on November 8, 2024 by Jtimes

Daga Yunusa Isa, Gombe

Gwamnan Jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya, ya yi ƙira da a gyara wassu hanyoyin gwamnatin tarayya da suka haɗe jihohin Arewa Maso Gabas don rage hatsura musamman a waɗannan watanni.

Gwamnan ya yi wannan kiran ne a lokacin da ya ƙaddamar da gangamin kiyaye hatsura a watannin ƙarshen shekara na bana, tare da taron tattaunawa wadda Hukumar Kiyaye Hatsura ta Ƙasa (FRSC) Reshen Jihar Gombe ta shiryawa masu ruwa da tsaki a Babbar Tashar Mota ta Ibrahim Hassan Dankwambo.

Gwamnan wanda Kwamishinan Ayyuka, Gidaje da Sufuri Injiniya Usman Maijama’a Kallamu ya wakilta, yace hanyoyin suna da muhimmanci ga miliyoyin ‘yan Najeriya dake jihohi shida na yankin, kuma sun kasance tamkar gadar dake haɗe yankin da sauran sassan ƙasar nan.

Yace hanyoyin musamman na Gombe zuwa Bauchi, da Gombe zuwa Dukku, da Gombe zuwa Biu, da Gombe zuwa Potiskum da kuma wassu sassan hanyar Gombe zuwa Yola suna ƙara zama tarkon mutuwa ga matafiya musamman a irin waɗannan watanni huɗu na ƙarshen shekara, inda ya yi ƙira ga gwamnatin tarayya ta hannun ma’aikatar ayyuka ta yi dukkanin mai yiwuwa don daƙile matsalar.

Da yake yabawa hukumar ta FRSC bisa jajircewarta wajen rage hatsura, gwamnan yace gwamnatinsa ta cimma nasarar fiye da kaso 70 cikin 100 a shirinta na Network Eleven Hundred, inda ake yiwa kowace ƙaramar hukuma hanyoyi aƙalla kilomita 100-100 don inganta zirga-zirga tsakanin birane da yankunan karkara.

Da yake magana kan taken gangamin magance hatsuran na bana; wato “Yi Magana Kan Tuƙin Ganganci: Hatsura Suna Kashe Fasinjoji Fiye da Direbobi”, Gwamnan ya buƙaci fasinjojin su riƙa sanya ido kan direbobi a yayin tuƙi.

A jawabinsa na maraba, Kwamandan Hukumar ta FRSC a Jihar Gombe Samson Ƙaura, yace hukumar ta ɓullo da sabbin dabaru don ganin an rage yawan hatsura a hanyoyin ƙasar nan.

Ya kuma yi kira ga direbobi su riƙe amanar fasinjoji, ta hanyar tabbatar da cewa motocinsu suna da lafiya, su guji shan giya ko ƙwaya kafin ko a lokacin tuƙi, kana su kasance masu bin dokoki da ƙa’idojin hanya.

Ƙaura ya ja hankalin fasinjoji su kai rahoton duk wani direban dake tuƙin ganganci ga ofishin hukumar ta FRSC mafi kusa ko wata hukumar tsaro data dace.

A nasa jawabin Babban Manajan Kamfanin Sufuri na Jihar Gombe da aka fi sani da Gombe Line, Dr Sani Sabo, ya jaddada ƙira ga Gwamnatin Tarayya kan ta gaggauta gyara hanyoyin na jihohin Arewa Maso Gabas don ceto rayukan direbobi dana fasinjoji.

Ya kuma yabawa gwamnatin jihar da hukumar ta FRSC da sauran masu ruwa da tsaki bisa jajircewar da suke yi na rage yawan hatsura a kan hanyoyin Jihar Gombe dana ƙasa baki ɗaya.

A saƙonninsu fatan alheri, wakilan hukumomin tsaro daban-daban, da shugabannin ƙungiyoyin sufuri, da sarakunan gargajiya, sun yabawa hukumar kiyaye hatsuran bisa jajircewarta kan rage hatsura, suna masu ƙira ga direbobi da fasinjoji su riƙa bin ƙa’idojin tafiye-tafiye.

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recent Posts

  • CAYEI calls for Urgent action to address climate change, biodiversity loss in Borno
  • FG Flags Off UBEC Stakeholders Meeting in Borno
  • Alleged Terrorism Financing: North-East Concerned Citizens Throw Weight Behind Gen. Buratai Condemn Gen. Ali Keffi
  • Borno schoolgirls trained to lead peace efforts in conflict-hit communities
  • Nutrition: SQ-LNS Formula Transforms Over 100,000 Children In Gombe

Recent Comments

  1. A WordPress Commenter on Hello world!

Archives

  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • June 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • February 2025
  • January 2025
  • December 2024
  • November 2024
  • October 2024
  • September 2024
  • August 2024
  • July 2024
  • June 2024
  • May 2024
  • April 2024
  • March 2024
  • February 2024

Categories

  • Agriculture
  • Anti Corruption
  • Article/Opinion
  • Cybercrime
  • Economy
  • Education
  • Environment
  • Governance
  • Health
  • Infrastructure
  • News
  • Nutrition
  • Opinion
  • Politics
  • Religion
  • Rural Development
  • Security
  • Tradition
  • Uncategorized
  • Urban Development
  • Urban Development
  • Women
  • Youths
©2025 Jewel Times | Design: Newspaperly WordPress Theme