Skip to content
Jewel Times
Menu
  • Gombe Social Investment Coordinator Visits Progress Radio, Seeks Collaboration
  • Sample Page
Menu

Gwamna Inuwa Ya Amince Da Sake Rabon Tallafin Abinci Ga Kananan Hukumomi Da Kungiyoyi

Posted on August 6, 2024 by Jtimes

 

A wani mataki na daƙile ƙalubalen tattalin arziƙin da al’ummar Jihar Gombe ke fuskanta a halin yanzu, Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya CON, ya amince da raba kayan abinci ga marassa galihu a faɗin jihar.

 

Hakan na kunshe ne ta cikin wata sanarwa da Babban Daraktan Yaɗa Labarun Gwamnan Jihar Ismaila Uba Misilli ya fitar tare da miƙawa Jewel Times Hausa.

 

Misilli yace hakan na zuwa ne bayan ƙudurin hakan da aka cimma a babban taron majalisar tsaron jihar da Gwamna Inuwa Yahaya ya jagoranta jiya Litinin.

 

Don haka Gwamnan ya amince da raba buhunan dawa dubu masu nauyin kilogiram 50-50 da buhunan shinkafa dubu masu nauyin kilogiram 25 da katon dubu na taliya ga kowace ƙaramar hukuma cikin ƙananan hukumomi 11 na Jihar Gombe.

 

Hakazalika, za a raba irin wannan tallafin abinci, buhuna 5,000 da katon-katon na taliya ga ƙungiyoyin addini, da ƙungiyoyin fararen hula, da ƙungiyoyin ɗalibai (GOSSA da NANS), da makarantun tsangaya da almajirai, da ƙungiyoyin matasa da mata da kuma masu buƙata ta musamman da sauran jama’a masu rauni a cikin al’umma.

 

Wannan dai shi ne karo na 19 da gwamnatin za ta raba irin wannan tallafi ga al’ummar Jihar Gombe a ci gaba da ƙoƙarin samar da agaji da inganta rayuwar al’ummar jihar a wannan mawuyacin lokaci.

 

Ana sa ran tallafin abincin zai taimaka matuƙa wajen rage wahalhalun da jama’a da dama ke fama da su a jihar, musamman ma masu rauni.

 

Gwamna Inuwa Yahaya, ya ƙara jajircewa wajen aiwatar da ingantattun matakan tallafawa jama’a don sauƙaƙa musu rayuwa a tsaka da fama da ƙalubalen tattalin arziƙin da ake ciki.

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recent Posts

  • Gombe Judge Steps Down From High-Profile Mechanic Village Land Dispute
  • Gombe Governor Receives New State NSCDC Commandant Idris Jibril
  • Gombe NSCDC Gets New Commander; Idris Jibrin
  • Billiri Easter Tragedy: Death Toll Rises to Six, 18 in Hospitals, 36 Inflicted
  • Amuga Condoles With Billiri Community, Supports Clarion Call by T.Y. Danjuma for Communities to Defend Themselves

Recent Comments

  1. A WordPress Commenter on Hello world!

Archives

  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • February 2025
  • January 2025
  • December 2024
  • November 2024
  • October 2024
  • September 2024
  • August 2024
  • July 2024
  • June 2024
  • May 2024
  • April 2024
  • March 2024
  • February 2024

Categories

  • Agriculture
  • Article/Opinion
  • Cybercrime
  • Economy
  • Education
  • Environment
  • Governance
  • Health
  • Infrastructure
  • News
  • Nutrition
  • Politics
  • Religion
  • Rural Development
  • Security
  • Tradition
  • Uncategorized
  • Urban Development
  • Urban Development
  • Women
  • Youths
©2025 Jewel Times | Design: Newspaperly WordPress Theme