Skip to content
Jewel Times
Menu
  • Gombe Social Investment Coordinator Visits Progress Radio, Seeks Collaboration
  • Sample Page
Menu

Civil Defence Ta Yi Holen Mutane 14 Bisa Zargin Kwacen Waya Da Badala A Gombe

Posted on February 17, 2024 by Jtimes

Daga Yunusa Isa, Gombe

Hukumar Tsaro Ta Civil Defence (NSCDC) Reshen Jihar Gombe ta yi holen wassu mutane 14 da take zargi da laifin ƙwacen waya da kuma lalata.

Da yake gabatar da waɗanda ake zargin, Kwamandan Hukumar a Jihar Muhammad Bello Muazu ta bakin Jami’in Hulɗa da Jama’a na Rundunar SC Buhari Sa’ad, yace an kama waɗanda ake zargin ne a gidajen saukar baƙi da otal-otal da tsakar dare a Gombe.

Yace biyo bayan haramcin da gwamnatin jihar ta sanya kan harkokin gidajen gala da kulob-kulob din dare, waɗanda ake zargin sun sauya akala zuwa wasu wurare, inda suke aikata munanan harkokinsu a gidajen baƙi.

Jami’in hulɗa da jama’an yace “Mun kama biyu daga cikin waɗanda muke zargin ne da laifin ƙwacen waya, wassu huɗu kuma a gidan Sifeta Hassan dake BCGA da misalin karfe 1:08 na dare, yayin da sauran takwas ɗin maza da mata kuma aka kama su ne a Travelers Lodge Gombe da misalin karfe 1:57 na dare, inda aka samu waɗanda ake zargin suna baɗala.

Da yake jaddada aniyar rundunar na daƙile ayyukan alfasha, da sauran laifuka a jihar, Buhari ya bukaci goyon bayan al’ummar jihar don kakkaɓe bata gari a jihar.

Ya ƙara da cewa da zarar an kammala bincike za a gurfanar da waɗanda ake zargin a gaban kotu don su fuskantar hukunci.

Wasu daga cikin waɗanda ake zargin, sun danganta abinda suka aikata da son zuciya da ruɗin shaiɗan, suna masu alƙawarin kauracewa irin wannan alfasha, tare da zama na gari a cikin al’umma.

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recent Posts

  • Gombe NUJ Hails Gov Yahaya Over Electricity Sector Reforms
  • Alleged Terrorism Financing: Bauchi Assembly Dismisses EFCC Claims, Calls For Democratic Freedom
  • Rear Admiral Njiddari Commends Gombe Governor On Balanga Power Project, Infrastructure
  • Bauchi Journalists Unveil Book On Life, Legacies Of Late Dahiru Bauchi
  • Gombe Revenue Tribunal Pledges Efficient, Fair Tax Justice In 2026

Recent Comments

  1. A WordPress Commenter on Hello world!

Archives

  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • June 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • February 2025
  • January 2025
  • December 2024
  • November 2024
  • October 2024
  • September 2024
  • August 2024
  • July 2024
  • June 2024
  • May 2024
  • April 2024
  • March 2024
  • February 2024

Categories

  • Agriculture
  • Anti Corruption
  • Article/Opinion
  • Cybercrime
  • Economy
  • Education
  • Environment
  • Governance
  • Health
  • Infrastructure
  • News
  • Nutrition
  • Opinion
  • Politics
  • Religion
  • Rural Development
  • Security
  • Tradition
  • Uncategorized
  • Urban Development
  • Urban Development
  • Women
  • Youths
©2026 Jewel Times | Design: Newspaperly WordPress Theme