Skip to content
Jewel Times
Menu
  • Gombe Social Investment Coordinator Visits Progress Radio, Seeks Collaboration
  • Sample Page
Menu

NNPP Ta Janye Daga Shiga Zaben Kananan Hukumomi A Gombe

Posted on April 27, 2024 by Jtimes

Daga Yunusa Isa, Gombe

Jam’iyyar NNPP reshen Jihar Gombe ta janye daga shiga zaɓen ƙananan hukumomin da za a yi ranar Asabar ɗin nan.

Da yake jawabi a yayin gabatar da tutoci ga ‘yan takarar shugabancin ƙananan hukumomi da kansiloli a Gombe, Shugaban Jam’iyyar na Jiha Barista Rambi Ibrahim Ayala, yace NNPP ta yanke shawarar janye shiga zaɓen ne har sai an yi gyare-gyaren kundin tsarin mulki don baiwa ƙananan hukumomi yancin cin gashin kansu tare da baiwa hukumar zaɓe ta ƙasa INEC damar gudanar da zaɓukan ƙananan hukumomi.

Yace sun kuma yanke shawarar kin shiga zaɓen ne saboda wasu dalilai da ke nuna cewa jam’iyya mai mulki da hukumar zaɓe ta jihar ba su nuna ƙudurin gudanar da zaɓen a jihar ba.

Rambi ya yi zargin cewa jam’iyya mai mulki a wassu lokuta ta bayyana ƙarara cewa babu shakka ‘yan takararta ne za su lashe zaɓen.

A nasa jawabin jagoran jam’iyyar kuma ɗan takararta na gwamna a zaɓen 2023 Hon. Khamisu Ahmad Mailantarki, ya bayyana ƙwarin gwiwar cewa ganin yadda jam’iyyar take da cikakken tsarin shugabanci a faɗin gundumomi 114 na jihar, ko shakka babu NNPP ce za ta lashe zaɓen 2027.

Da yake ƙarfafawa ’yan jam’iyyar gwiwa kan haɗin kai, kishin ƙasa da jajircewa, Mailantarki ya ba da tabbacin cewa jam’iyyar na da kyakkyawan matsayi na kafa gwamnati mai zuwa a jihar.

Da yake jawabi a madadin ‘yan takaran da aka baiwa tuta, ɗan takaran shugaban karamar hukumar Gombe a jam’iyyar, Adamu Babale Makera, ya bayyana goyon baya ga matsayin jam’iyyar na kin shiga zaɓen.

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recent Posts

  • BOGIS Directs Land Owners To Link NIN With Certificates Of Occupancy
  • Gombe Wins 10th Edition of NILDS Zonal Quiz Competition
  • Gombe Civil Service Commences Staff Verification, Aims Digital Database
  • Merit and Vibes Awards 2025 Celebrates Excellence, Promotes Inclusion in Creative Industry
  • Gombe Adopts Digital Technology to Improve Education Data Collection for 2024/2025 School Census

Recent Comments

  1. A WordPress Commenter on Hello world!

Archives

  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • June 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • February 2025
  • January 2025
  • December 2024
  • November 2024
  • October 2024
  • September 2024
  • August 2024
  • July 2024
  • June 2024
  • May 2024
  • April 2024
  • March 2024
  • February 2024

Categories

  • Agriculture
  • Anti Corruption
  • Article/Opinion
  • Cybercrime
  • Economy
  • Education
  • Environment
  • Governance
  • Health
  • Infrastructure
  • News
  • Nutrition
  • Opinion
  • Politics
  • Religion
  • Rural Development
  • Security
  • Tradition
  • Uncategorized
  • Urban Development
  • Urban Development
  • Women
  • Youths
©2025 Jewel Times | Design: Newspaperly WordPress Theme