Skip to content
Jewel Times
Menu
  • Gombe Social Investment Coordinator Visits Progress Radio, Seeks Collaboration
  • Sample Page
Menu

Za A Fara Karatu A Tsangayar Kimiyyar Muhalli Ta GSU Dake Dukku

Posted on February 15, 2024 by Jtimes

Daga Yunusa Isa, Gombe

Jami’ar Jihar Gombe (GSU) ta bayyana cewa nan ba da daɗewa ba za a fara karatu a reshenta dake Dukku a matsayin Tsangayar Kimiyyar Muhalli.

Shugaban Majalisar Gudanarwar Jami’ar Sanata Joshua Lidani ne ya bayyana haka yayin wani taron manema labarai kan nasarorin da jami’ar ta cimma.

Lidani yace, “Biyo bayan amincewar da Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya ya yi na kafa tsangayar jami’ar a makarantar da aka tsara tun farko a matsayin kwalejin jinya a Dukku, yanzu haka an kammala aikin inda reshen zai fara aiki a matsayin Tsangayar Kimiyyar Muhalli na Jami’ar Jihar Gombe. Za a ɗauki sabin ɗalibai a tsangayar nan gaba kaɗan.”

Da yake yabawa gwamnatin jihar bisa farfaɗo da fannin ilimi, shugaban yace makarantun sakandaren jihar da aka inganta, da sabin manyan makarantu biyar da aka ƙirƙiro zasu riƙa samarwa GSU da sauran jami’o’i ɗalibai masu nagarta.

Da yake tsokaci kan nasarorin da jami’ar ta cimma, Sanata Joshua Lidani yace majalisar gudanarwar jami’ar ta amince da ƙarin girma wa malamai 107, inda 4 daga cikinsu suka zama farfesoshi, 18 kuma zuwa matsayin ‘reader’, yayin da wasu 85 suka samu ƙarin girma zuwa matakai daban-daban.

Yace majalisar ta kuma amince da ƙarin girma wa ma’aikatan da ba malamai ba su 57 zuwa mutakai daban-daban.

Shugaban ya yabawa Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya bisa haɗin kai da goyon bayan da yake baiwa jami’ar, lamarin da yace ya sa jami’ar ta GSU ta yi fintinkau ga sa’ointa a Najeriya.

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recent Posts

  • Bala Wunti Support Organisation Empowers Blind, Deaf with Entrepreneurial Skills
  • NEDC Bolsters Journalists’ Welfare with Ramadan Food Support
  • Ramadan: BWSO Donates Cash, Food Items to People with Disabilities in Bauchi
  • Gana Aliyu Emerges Gombe IPAC Chairman as New Executive Council Takes Office
  • FRSC Issues Red Alert as Haze Envelopes Gombe Roads

Recent Comments

  1. A WordPress Commenter on Hello world!

Archives

  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • June 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • February 2025
  • January 2025
  • December 2024
  • November 2024
  • October 2024
  • September 2024
  • August 2024
  • July 2024
  • June 2024
  • May 2024
  • April 2024
  • March 2024
  • February 2024

Categories

  • Agriculture
  • Anti Corruption
  • Article/Opinion
  • Cybercrime
  • Economy
  • Education
  • Environment
  • Governance
  • Health
  • Infrastructure
  • News
  • Nutrition
  • Opinion
  • Politics
  • Religion
  • Rural Development
  • Security
  • Tradition
  • Transportation
  • Uncategorized
  • Urban Development
  • Urban Development
  • Women
  • Youths
©2026 Jewel Times | Design: Newspaperly WordPress Theme