Skip to content
Jewel Times
Menu
  • Gombe Social Investment Coordinator Visits Progress Radio, Seeks Collaboration
  • Sample Page
Menu

Cin Zarafi: Gwamnan Gombe Ya Kori Masu Taimaka Masa Hudu Da Aka Zarga Da Cin Zarafin Kansila

Posted on December 23, 2025 by Jtimes

 

Gwamnan Jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya, ya amince da korar Adamu Abdullahi Danko da wassu mataimaka uku nan take bayan binciken cin zarafin da aka yiwa Hon. Abdulrahman Abubakar Sheriff, Kansila mai wakiltar gundumar Shamaki a Ƙaramar Hukumar Gombe.

 

Wata sanarwa da Babban Daraktan Yaɗa Labarunsa Ismaila Uba Misilli ya fitar tace matakin wadda Sakataren Gwamnatin Jihar Farfesa Ibrahim Abubakar Njodi ya sanar, ya biyo bayan kafa kwamitin bincike na musamman ne kan lamarin.

 

Sakamakon binciken kwamitin wanda rahotannin hukumomin tsaro suka tabbatar ne ya kai ga matakin da Gwamnan ya ɗauka.

 

A cewar Sakataren Gwamnatin Jihar, masu taimakawa gwamnan da abin ya shafa sune: Adamu Abdullahi Danko – Babban Mataimaki na Musamman na 2 kan Harkokin Cikin Gida, da Garba Mohammed Mai Rago – Babban Mataimaki na Musamman na 2 kan harkokin Siyasa, da Rabiu Sulaiman Abubakar – Babban Mataimaki na Musamman na 2 kan Kafafen Sada Zumunta na Zamani da kuma Ali Ibrahim Baban Kaya – Babban Mataimaki na Musamman na 2 kan Hulɗa da al’umma).

 

Gwamna Inuwa Yahaya ya bada umarnin cewa korar ta fara aiki ne nan take.

 

An kuma umurci duk jami’an da abin ya shafa su miƙa duk kadarorin gwamnati dake hannunsu ga hukumomin da suka dace ba tare da wani ɓata lokaci ba.

 

Gwamna Inuwa Yahaya ya sake jaddada cewa gwamnatinsa ba za ta lamunci tashin hankali, rashin ɗa’a da cin zarafi ba, yana mai cewa ba zai lamunci duk abinda zai iya yin barazana ga zaman lafiyar jama’a ko lalata amincin da gwamnatinsa ke da shi a idon al’ummar jihar ba.

 

Ya tabbatarwa al’ummar Jihar Gombe jajircewar gwamnatinsa wajen bin doka da oda, riƙon amana da kuma zaman lafiya. Ya ƙara da cewa za a ɗauki matakai masu tsauri don kare zaman lafiya da ɗorewar kwanciyar hankalin da jihar take ta fafutukar ɗabbaƙawa.

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recent Posts

  • Bauchi SUBEB Begins Renovation Of Dilapidated Schools
  • When Honour Finds Its Owner Muhammad Jabdo, Mukaddam of Misau
  • Christmas: Loyalist To Chief Whip Supports Less Privileged With Foodstuff, Seasonings In Billiri
  • Cin Zarafi: Gwamnan Gombe Ya Kori Masu Taimaka Masa Hudu Da Aka Zarga Da Cin Zarafin Kansila
  • GOSUPDA Refutes Allegations Of Illegal Reallocation Of Land In Gombe

Recent Comments

  1. A WordPress Commenter on Hello world!

Archives

  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • June 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • February 2025
  • January 2025
  • December 2024
  • November 2024
  • October 2024
  • September 2024
  • August 2024
  • July 2024
  • June 2024
  • May 2024
  • April 2024
  • March 2024
  • February 2024

Categories

  • Agriculture
  • Anti Corruption
  • Article/Opinion
  • Cybercrime
  • Economy
  • Education
  • Environment
  • Governance
  • Health
  • Infrastructure
  • News
  • Nutrition
  • Opinion
  • Politics
  • Religion
  • Rural Development
  • Security
  • Tradition
  • Uncategorized
  • Urban Development
  • Urban Development
  • Women
  • Youths
©2025 Jewel Times | Design: Newspaperly WordPress Theme